Tinubu ya haramta wa ministocinsa tafiye-tafiye zuwa kasashen ketare

 

Tinubu ya haramta wa ministocinsa tafiye-tafiye zuwa kasashen ketare


Shugaban Nijeriya Bola Tinubu ya bayar da umurnin haramta wa ministocinsa da sauran mukarraban gwamnatinsa tafiye-tafiye zuwa kasashen waje.

Shugaba Tinubu ya ba da umurnin ne ta cikin wata wasika da shugaban ma’aikatansa, Femi Gbajabiamila, ya aike wa sakataren gwamnatin tarayya, George Akume.

A cikin wasikar, mai kwanan wata 12 ga Maris, 2024, Tinubu ya ba da umurnin hana duk wasu  tafiye-tafiye zuwa kasashen waje.

Sai dai ya ce an keɓance tafiyar da ta zama wajibi.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp