Gwamnatin tarayya ta yi kira ga kungiyoyin manyan ma’aikatan jami’o’in kasar, SSANU, daNASU, da su janye yajin aikin gargadi na kwanaki bakwai da suka fara gudanarwa a ranar Litinin.
Karamar ministar kwadago da samar da nagartar aiki Nkeiruka ce ta yi wannan roko a cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun Daraktan yada labarai da hulda da jama’a na ma’aikatar, Olajide Oshundun a ranar Litinin a Abuja.
Idan dai ba a manta ba kwamitin hadin gwiwa na kungiyoyin biyu wato SSANU da NASU sun umurci mambobinsu da su shiga yajin aikin gargadi na kwanaki bakwai kan rashin biyansu albashin watanni hudu da suke bin gwamnati bashi.