Gwamnatin Kaduna ta ce ta ceto daliban Kuriga gaba dayansu


A cikin wata sanarwa da Gwamna Uba Sani ya sanya wa hannu, ta yi godiya ga shugaban kasa da jami'an bisa abin da ya ce namijin kokarin da suka yi na ganin an kubutar da daliban ba tare da sun yi ko kwarzane ba.

Duk da dai a sanarwar, Gwamnan bai yi bayanin hanyoyin da aka bi aka ceto daliban ba, amma ya ci gaba da godiya har ga mai ba shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, Malam Nuhu Ribadu da sojoji da daukacin al'ummar Nijeriya da suka yi ta addu'o'in ganin daliban sun kubuta.

A ranar 7 ga wannan wata na Maris ne dai 'yan bindiga suka shiga makarantar firamaren garin Kuriga na karamar hukumar Chikun a jihar Kaduna suka yi awon-gaba da dalibai kusan 287.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp