Gwamna Dauda Lawal ya yi kira da a ƙara yawan sojoji zuwa jihar Zamfara.

 Gwamna Dauda Lawal ya yi kira da a ƙara yawan sojoji zuwa jihar Zamfara.


A ranar litinin ne gwamnan ya ziyarci babban hafsan tsaron ƙasa, Janar Christopher Gwabin Musa, a hedikwatar tsaro da ke Abuja.


A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun Gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ta bayyana cewa gwamnan ya gana da hafsan tsaro domin tattauna matsalar tsaro data addabi  jihar Zamfara.


Gwamna Lawal ya bayyana damuwarsa bisa yadda 'yan bindiga suka addabi jihar,ya kuma yi kira ga babban hafsan hafsoshin tsaron kasar da ya tura ƙarin jami'an soji da kayan aiki na zamani da suka dace a jihar.



Gwamnan ya bayyana cewa jihar tana fama da karancin jami'an tsaro ga kuma matsalar 'yan bindinga masu garkuwa da mutane domin biyan kudin fansa,hakan yasa manoma ba sa iya noma gonakinsu, ga hare-haren da ake ci gaba da kaiwa na janyo asarar rayuka da dama.


Inda yace bisa wannan dalilai al'umma na shan wahala,domin kusan koyaushe 'yan bindinga na kokarin kai hare hare a yankuna dadama,hakan yasa muke fatan cewa za'a duba koken mu domin samun zaman lafiya mai dorewa a jihar.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp