Ƙudirin kafa yan sandan jihohi ya tsallake karatu na biyu a majalisa


Majalisar wakilai ta amince da kudirin dokar karatu na biyu, daftarin da ke neman yin gyara ga kundin tsarin mulkin kasar na shekarar 1999 ta hanyar ba jihohi 36 na tarayyar kasar damar kafa ‘yan sandan jihohi.

A zaman majalisar na yau Talata an yi muhawara kan kudirin dokar da ke neman yin kwaskwarima ga kundin tsarin mulkin kasar na shekarar 1999, inda aka yi karatu na biyu.

Mataimakin kakakin majalisar, Benjamin Kalu da wasu mutane 14 suka dauki nauyin kudurin.

Post a Comment

Previous Post Next Post