Makamai milyan 200 ke hannun yan Nijeriya ba bisa ka’ida ba - Uba Sani 

 Makamai milyan 200 ke hannun yan Nijeriya ba bisa ka’ida ba - Uba Sani 



Gwamnan jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, ya koka kan yadda bindigu kusan miliyan 200 ke hannun yan Nijeriya da suka mallaka ba bisa ka'ida ba.


Gwamna Sani ya bayyana hakan ne a wata hira da gidan Talabijin na Channels TV Siyasar Lahadi.


Ya ce yaduwar bindigun ne ke haddasa tabarbarewar tsaro a kasar, inda ya yi kira da a sake duba dokar mallakar bindiga a kasar.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp