An fara zanga-zangar tsadar rayuwa a jihar Oyo

 An fara zanga-zangar tsadar rayuwa a jihar Oyo



Rahotanni daga garin Ibadan babban birnin jihar Oyo na cewa wasu matasa sun fito zanga-zanga kan tsadar rayuwa da ake fama da ita a fadin Nijeriya.


 Majiyar DCLHausa ta Nigerian Tribune ta ce matasan sun mamaye manyan titunan Ibadan dauke da kwalaye da rubutun cewa gwamnati ta hanzarta magance matsalar tsadar abinci.


 Nijeriya dai na cikin wani yanayi na tashin gwauron zabo da kayayyakin masarufi ke yi tun musamman ma a wannan shekarar ta 2024.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp