Ministan cikin gidan Nijar janar Toumba ya dauki wannan mataki a cikin wani kudurin doka da ya saka wa hannu a ranar 29 Janairun wannan shekara ta 2024 inda a ciki ya sanar da rushe wannan kungiya har sai baba ta gani
Ko da yake ministan bai sanar da dalilansa ba na daukan matakin amma ya maye gurbin membobin nata da sakatarorin ma'aikatar sa da ta sadarwa wadanda za su jagorancin aikin kungiyar na wani lokaci
To amma sai dai shugaban kungiyar ta Maison de la Presse Ibrahim Harouna ya ce basu da labarin wannan mataki domin kuwa basu samu takarda a hukumance da ta dakatar da ayyukan nasu duk kuwa da yadda take yawo a shafukan sada zumanta na zamani
Category
Labarai