Gwamnonin PDP sun bukaci a samar da yan sandan jihohi a Najeriya


Gwamnonin jam’iyyar PDP sun koka kan kalubalen tsaro da kasar ke fuskanta, inda suka yi kira ga gwamnatin tarayya da ta samar da yan sandan jihohi.

Gwamnonin sun yi wannan kira ne a jiya Alhamis a Jos, babban birnin jihar Filato lokacin da suka ziyarci gwamna Caleb Mutfwang, a gidan gwamnatin jihar, biyo bayan hare-haren da ‘yan bindiga suka kai, wanda ya yi sanadin asarar rayuka sama da 200 a cikin wata guda tare da lalata dukiyoyin na miliyoyin Nairori.

Gwamnonin da suka kai ziyarar sun hada da Seyi Makinde na jihar Oyo, Ahmadu Fintiri na jahar Adamawa da Peter Mbah na jihar Enugu da Godwin Obaseki na Edo da Ademola Adeleke na Jihar Osun.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp