Za a sake duba batun masarautun Kano – Kwankwaso

Sanata Rabiu Kwankwaso
Sanata Rabiu Kwankwaso

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran tafiyar Kwankwasiyya Sanata Rabiu Kwankwaso ya bayyana cewa za a sake duba batun masarautar jihar Kano.

Hakan dai na a cikin wata hira da manema labarai da yayi a ranar Alhamis. Idan zaku tuna tsohuwar gwamnatin da ta gabata ta raba masarautar Kano gida biyar, sana ta tsige Sarkin Kano Muhammadu Sanusi na biyu daga karagar mulki.

Tun bayan da kotun koli ta tabbatar da zaben Gwamnan jihar  Abba Yusuf Yusuf, jama’a ke ta kiraye-kiraye na a  dawo da tsohun Sarkin.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp