Hukumar Hisbah a jihar Kano takama mota dauke da barasa

 Hisbah a Kano ta kama mota makare da barasa 



Hukumar Hisbah a jihar Kano ta sanar da kama wata babbar mota makare da kwalaben barasa.


Hukumar ta kama motar a hanyar Zariya, ta kuma kama direban motar da wasu mutane biyu. 


Babban Daraktan Hukumar Hisbah ta Jihar Kano, Alhaji Abba Sufi, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na hukumar Malam  Ibrahim-Fagge ya sanya wa hannu a Kano.


“ Yace Motar da ke dauke da kwalabe daban-daban na barasa sama da 24,000 an kwace daga hannun ‘yan sumogal a hanyar Zariya da tsakar dare.


Jami'an Hisbah a jihar sun himmatu wajen yaki da shan miyagun kwayoyi da fasakwaurin barasa da sauran abubuwa masu sa maye a cikin jihar.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp