Gwamnatin Kogi ta dakatar da albashin ma'aikatan 231. d

 Gwamnatin Kogi ta dakatar da albashin ma'aikata 231.



Gwamnatin jihar Kogi ta dakatar da biyan albashin ma’aikata 231 na ma’aikatan jihar bisa zargin kin bin umarnin gwamnati na sabunta bayanan su ga gwamnatin .


Shugabar ma’aikatan jihar (HOS), Hannah Odiyo, ta bayyana hakan Lokoja babban birnin jihar a wajen bikin kaddamar da katin shaida ga ma’aikatan jihar.


Odiyo tace ce ma’aikatan da abin ya shafa sun kasa bin umarnin gwamnatin jihar Kogi na sabunta bayanan su.


Hakan yasa hukumar ta dakatar da biyan albashin ma’aikatan da abin ya shafa tun watan Nuwamba 2023 har zuwa yau.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp