Gwamnatin Nijeriya ta koka kan cewa sai ta yi 'yan dabaru sannan take iya biyan albashin ma'aikata domin babu kudi a kasa.
Ministan kasafin kudi da tsare-tsare na kasa Atiku Bagudu ne ya bayyana haka ga manema labarai a Abuja.
Bagudu ya bayyana cewa kasar ta riga ta faɗa cikin wani irin matsanancin matsin tattalin arziƙi unda take fuskantar manya-manyan kalubalen ƙarancin samun kuɗaɗen shiga.