Sabbin nade-naden Tinubu ba su kawar da kyamar da yake nuna wa arewa ba - Mahadi Shehu


Ga videon wannan rahoto: 


 

Ruwan mukamai ne dai Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya yi wa mutanen da suka fito daga arewacin Nijeriya a baya-bayan nan. Kama daga jagorancin hukumar alhazai ta kasa zuwa hukumar PTDF wadda ke tura matasan Nijeriya karatu kasashen ketare ta amfani da  rarar kudaden da gwamnati ta samu a harkar man fetur zuwa hukumar NCC mai sanya ido kan harkoki na sadarwa da kuma hukumar ICPC mai yaki da rashawa a Nijeriya, dukkaninsu Shugaba Tinubu ya damka su a hannun mutanen arewa. Sai dai a cewar, Mahadi Shehu, wanda ya jima yana zargin gwamnatin Tinubu da fifita kabilar Yarbawa a wajen nada mukamai, wadannan nade-nade ba su gyara kyamar da Mahadin ke zargin Tinubu da nuna wa mutanen arewa ba.

Sai dai gwamnatin Tinubu ta ce babu adalci a cikin irin wannan fahimta ta Mahadi Shehu. Abdulaziz Abdulazi da ke magana da yawun Shugaba Tinubu ya ce zafin shan kaye a zabe ne ke sanya irinsu Mahadi Shehu sukar gwamnatin ta APC.

Duk da cewa tun a zamanin mulkin mallaka ne dai manyan kabilun Nijeriya suka fara nuna wa juna rashin amincewa a wajen rabon mukami, har yanzu matsalar taki ci, taki cinyewa, a cewar Ibrahim Baba Shatambaya, malamin jami’ia da ke  sharhi a kan lamurran siyasa a Nijeriya.

A yayin da masu adawa da salon nade-naden gwamnatin Tinubu ke ci gaba da matsa mata lamba, masu sharhi na aza ayar tambaya a kan, shin mutanen arewa suke son  gani a shugabanci ko da  ba za su iya tabuka wani abu ba ko kuwa mutanen da za su kawo ci gaba a Nijeriya, tun da a baya an ba ‘yan arewa mukamai masu gwabi kuma ba a ga wani cci-gaba ba?

Masu sharhi dai sun tsura ido su ga ko wadanda Shugaba Tinubun ya nada mukamai dabam-dabam za su tabbatar da zargin ‘yan adawa na danne yankin arewacin Nijeriya a wajen zuba ayyukan gwamnati ko kuma za su bai wa mara da kunya.

 

DCL Hausa

Aisha Usman Gebi

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp