Mutane milyan 283 na kwana da yunwa a Nahiyar Afrika - Adesina

Shugaban bankin bunkasa Nahiyar Afrika Dr Akinwumi Adesina ya sanar cewa mutane milyan 283 na kwana da yunwa a Nahiyar Afrika.

Dr Adesina na magana ne a taron daidaita farashi a kasar Amurka, inda ya ce bankin ya ware wasu kudi Dala bilyan 1 don tallafar jihohi 24 na Nijeriya.

Ya ce hakan wani kari ne daga Dala Milyan 520 da aka tura don inganta aikin gona da zummar abinci ya wadata.

Shugaban bankin ya ce an yanke shawarar kai wannan dauki a Nijeriya don a bunkasa sassan aikin gona saboda yawan kasar noma da Allah Ya huwace mata.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp