Zulum zai daure 'yan bangar siyasa shekaru 7 a gidan kaso



Gwamnan jihar Borno Prof Babagana Umara Zulum ya sa hannu kan dokar da za ta ba da a daure duk wanda aka samu laifin bangar siyasa a jihar.

Gwamnan ya sa hannu kan dokar ne tare da karin wasu dokoki 8 da majalisar dokokin jihar ta amince da su.

Gwamnan ya ce an dauki wannan matakin ne domin dakile yawan matsalolin bangar siyasa da yi wa yara kanana fyade a jihar.

Prof Babagana Umara Zulum ya ce bayan wannan hukunci na daurin shekaru 7. Sannan masu daukar nauyin su ma ba za a bar su haka nan ba, sai an hukunta su.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp