Shugaban Zimbabwe ya nada 'ya'yansa biyu mukamin minista a gwamnatinsa


Shugaban kasar Zimbabwe Emmerson Mnangagwa ya nada dan cikinsa David Kudakwashe Mnangagwa mukamin karamin minista bayan sake zabensa da aka yi a matsayin shugaban kasar.

Wannan nadi dai ya tayar da kura a siyasar kasar, inda wasu ke zargin shugaban kasar da nadin 'yan'uwa da abokan arziki a gwamnatinsa.

An nada David Kudakwashe Mnangagwa mai shekaru 34 a mukamin karamin ministan kudi a yayin da aka nada Tongai Mafidhi, da ga dan'uwan shugaban a matsayin karamin ministan shakatawa na kasar.

Emmerson Mnangagwa dai ya ayyana sunayen mutane 26 da ya nada mukaman ministoci a sabuwar gwamnatin.

A shekarar 2017 dai ne aka fara zaben Mnangagwa mai shekaru 80 a matsayin kasar Zimbabwe.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp