Daraktan sufuri a Nijar ya halaka kanshi





Daraktan sufuri a jihar Tillaberi ta Jamhuriyar Nijar Adamou Halidou ya halaka kansa, inda ya mutu ta hanyar rataye kansa a saman bishiya.

Adamou Halidou wanda dan asalin garin Dogon Doutchi ne na jihar Dosso ta kasar ya rataye kansa a wata bishiya a ranar Larabar nan.
Daraktan sufuri a Nijar dai, kwantankwacin kwamishina ne a mukaman da ake rabawa a jihohin Nijeriya.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp