Ba zan ba ku kunya ba, Tinubu ya tabbatar wa 'yan Nijeriya


Zababben shugaban Nijeriya Bola Ahmad Tinubu ya ce ba zai ba 'yan kasar kunya ganin yadda suka aminta suka zabe shi.

Bola Tinubu na magana ne bayan da shugaba Buhari ya lakaba masa kambin girmamawa na GCFR a fadar shugaban kasa, Abuja.
Ya ce ya san muhimmancin girmamawa da irin kalubalen da ke gabansa. Inda ya sha alwashin cewa ba zai ba 'yan Nijeriya kunya ba.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp