'Yan Nijeriya miliyan 82 na iya fuskantar yunwa nan ba da jimawa ba, in ji MDD

 'Yan Nijeriya miliyan 82 na iya fuskantar yunwa nan ba da jimawa ba, in ji MDD


Majalisar Dinkin Duniya ta yi hasashen cewa ‘yan Nijeriya miliyan 82, kusan kashi 64 cikin 100 na al’ummar kasar za su iya fama da yunwa nan da shekara ta 2030, inda ta yi kira ga gwamnati da ta magance matsalolin da kasar ke fuskanta.


Hasashen ya zo ne sakamakon hauhawar farashin kayan abinci da ake ci gaba da yi a kasar.


A cewar hukumar kididdiga ta kasa, hauhawar farashin kayan abinci a Nijeriya ya kai sama da kashi 40.66 cikin 100 a watan Mayun 2024, wanda ya zarce na watan da ya gabata.



A shekarar 2023, hukumar abinci da aikin noma ta yi hasashen cewa akalla ‘yan Nijeriya miliyan 2.6 a jihohin Borno, Sokoto da Zamfara, da kuma Abuja na iya fuskantar matsalar abinci tsakanin watan Yuni zuwa Agusta 2024.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp