'Yan bindiga sun kashe Sakataren jam'iyyar PDP a jihar Zamfara
'Yan bindiga sun kashe Sakataren jam'iyyar PDP na karamar hukumar Tsafe a jihar Zamfara.
Shugaban jam’iyyar PDP na karamar hukumar Garba Garewa ne ya tabbatar da kisan sakataren na jam’iyyar a Tsafe ga gidan talabijin na Channels ranar Talata.
"Muna zargin wadanda suka kashe shi 'yan fashi ne, sun shiga gidansa jiya (Litinin) suka harbe shi," in ji Garewa.