Kungiyoyin matasa a a jihar Ogun sun bukaci shugaba Tinubu ya bude boda

 Kungiyoyin matasa a a jihar Ogun sun bukaci shugaba Tinubu ya bude boda




Gamayyar kungiyoyin matasan jihar Ogun sun yi kira ga shugaban kasa Bola Tinubu da ya bude dukkanin iyakokin kasa a wani mataki na magance matsalar tsadar abinci da yadda za a kara habaka tattalin arziki da kasar.


Kakakin kungiyar, Fẹmi Owoẹye, wanda ya yi wa manema labarai jawabi a Abeokuta, ya roki Tinubu da ya tashi tsaye wajen shawo kan matsalar ta hanyar bude iyakokin kasa domin bunkasa tattalin arziki da rage tsadar kayan abinci.


Matasan sun kuma nuna damuwarsu kan cewa duk matakan da gwamnati kasar ta bijiro don magance wahalhalun da ake fama da su ba su shafi matasan Nijeriya ba, musamman ma wadanda ba su da aikin yi.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp