Har yanzu ba'a fara bamu albashin watanni hudu da gwamnati ta rike mana ba-ASUU

Kungiyar Malaman Jami’o’i ta kasa ASUU ta ce har yanzu ba a fara sakin Albashin watanni 4 da shugaban kasa Bola Tinubu ya umurci a biya su.

Kimanin watanni biyu cif-cif tun bayan da shugaban Nijeriya Bola Tinubu ya amince da a saki albashin watanni hudu da aka hana malaman jami'o'in Nijeriya sakamaon yajin aikin da suka tsunduma, kungiyar malaman jami'o'i ta (ASUU) ta ce har yanzu mambobinta ba su karbi albashin ba.

Shugaban kungiyar ta ASUU, Farfesa Emmanuel Osodeke ya ce har yanzu gwamnati ba ta  aiwatar da mafi yawan bukatun da suka yi jarjejeniyar za a biya wa ya'yanta.

Wannan na zuwa ne bayan da yan kungiyar ta ASUU suka rika korafi kan yadda kudaden tafiyar da majalisun dokokin kasar biyu ya zarta wanda aka ware musu cikin kasafin kudin bana.


 

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp