Shehu Sani ya fadi dalilin barinsa PDP ya koma APC


Tsohon Sanatan jihar Kaduna Shehu Sani ya ce Gwamnan Kaduna Uba Sani ne ya yi sanadiya komawar sa jam’iyyar APC, bayan wani zaman sulhu a jihar.

Dan gwagwarmayar ya tabbatar da cewa yana cikin wadanda suka kafa jam’iyyar APC a jihar Kaduna kuma ya bayar da gudunmawa wajen dora jam’iyyar a kan turba.

Da yake zantawa da gidan talabijin na Channels, Shehu Sani ya kuma bayyana cewa takun-saka da ta shiga tsakaninsa da tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, ita ce ta yi sanadin fitar sa jam'iyyar a baya.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp