Saudiyya ta bai wa jihar Kano da wasu jihohin arewa tallafin dabino tan 50


Hukumomin kasar Saudiyya sun raba tan 50 na dabino ga jihar Kano da wasu jihohin arewacin kasar, baya ga irin wannan tallafin na tan 50 da ta bayar a Abuja.

A cewar wata sanarwa da ofishin jakadancin Saudiyya da ke Abuja ya fitar, tallafin wani bangare ne na aikin alherin da kasar ke yi shekara-shekara, karkashin cibiyar ba da agajin jin kai da jin kai ta Sarki Salman (KSrelief).

Tallafin na da manufar taimakawa mabukata a fadin Nijeriya da kuma karfafa dankon zumunci tsakanin kasashen biyu.

 

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp