Cire tallafin man fetur munyi shi ne da kyakyawar manufar kare makomar matasan Nijeriya - Shugaba Tinubu

Shugaba Bola Ahmad Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu ya ce duk wani mataki da ya dauka har zuwa yanzu, ciki har da batun cire tallafin man fetur ya shafi matasan Nijeriya ne da kuma makomar su.

Tinubu ya bayyana haka ne a lokacin kaddamar da kwamitin tsare-tsare na taron matasa na kasa a fadar gwamnati da ke Abuja.

Ya ba da tabbacin cewa, an yi gyare-gyaren tattalin arzikin ne domin karfafa tattalin arzikin kasar don samar da wadata ga matasan Nijeriya, wadanda su ne sama da kashi 60 cikin dari na al’ummar kasar.

Ya tabbatar da cewa matasa sune fatan Nijeriya, kuma komai ya rataya a kan su, da ya ce duk shawarar da ya yanke saboda matasan ne ciki harda cire tallafin man fetur don kare makomar su.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp