Za a yi tsananin zafin Rana daga Asabar zuwa Litinin - Hukumar hasashen yanayi ta Najeriya Nimet


Hukumar hasashen yanayi ta Najeriya NIMET ta ce za a samu tsananin zafi da kwallewar rana daga Asabar 22 zuwa Litinin 24 ga Fabrairu 2025.

Hukumar ta ce za a samu hasken tare da yanayin Hazo a wasu sassan Arewacin kasar, yayin da za a samu kadawar Iska a wasu jihohin Arewa ta Tsakiya da Kudancin kasar.

Daga cikin jihohin da za a samu yanayin Hazo da Rana akwai Nassarawa sai Plateau da Kogi da Benue sai birnin Tarayya Abuja.

A kudancin kasar kuwa za a samu hadari da tsawa a jihohin Lagos, Delta sai Cross River.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp