'Yan Nijeriya na korafi akan cin hanci amma kuma suna kare gurbatattun shugabanni - Shugaban hukumar EFCC


Shugaban hukumar yaki da cin hanci da rashawa a Nijeriya Ola Olukoyede, ya ce 'yan Nijeriya na tsinuwa ga cin hanci amma kuma su rika goyon bayan gurbatattun shugabannin da aka gurfanar a gaban kotu.

Olukoyede ya ce kasar nan za ta fita daga kangin da take ciki idan har kowane dan kasa zai yaki cin hanci a duk inda aka aikata shi.

Shugaban na EFCC ya bayyana hakan ne a lokacin da ya karbi bakuncin shugabannin cibiyar naƙaltar sadarwa lokacin tarzoma suka kai masa a Abuja.


 

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp