'Yan bindiga sun yi garkuwa da wasu dalibai mata 4 a jihar Benue

 


Rundunar ‘yan sandan jihar Benue ta tabbatar da sace dalibai mata 4 na jami’ar aikin gona ta gwamnatin tarayya da ke Makurdi.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Benue, CSP Sewuese Anene, ya tabbatar da faruwar lamarin a wata tattaunawa ta wayar tarho da gidan talabijin na Channels, inda ya ce an fara gudanar da bincike tare da nemo inda suke.

Wasu majiyoyi a kusa da jami'ar sun ce wasu 'yan bindiga sun yi garkuwa da daliban ne a harabar jami’ar da misalin karfe 8:30 na dare, lamarin da ya haifar da firgici ga daliban.

Yace daliban da aka yi garkuwa da su sun hada da, Emmanuella Oraka, Fola, Susan da kuma Ella.

A halin da ake ciki dai labarin sace daliban ya haifar da zanga-zanga daga daliban da suka zagaye makarantar inda suka bukaci mahukuntan makarantar su dauki matakin gaggawa.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp