Tinubu ya sauke shugabar jami'ar Abuja Farfesa Aisha Maikudi




Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya sauke Aisha Maikudi  mataimakiyar shugabar jami’ar Abuja, wadda a yanzu ake kira da Jami’ar Yakubu Gowon.

An sanar da sauke Aisha Maikudi  sa’o’i kadan bayan da ta jagoranci bikin yaye dalibai da suka kammala karatun digiri a makarantar.

Dama dai ana ta  cece-kuce game da nadin nata inda wasu malaman jami'ar ke cewa, ta hau wannan mukamin ba bisa ka'ida ba, kamar yadda jaridar Daily Trust ta rawaito.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp