Rundunar yan sandan Nijeriya ta ce ba lokacin Sufetan yan sanda Egbetokun makamai 3,907 suka yi ɓatan dabo ba


Rundunar 'yan sandan Nijeriya ta ce makamai 3,907 da ake bincike sun yi ɓatan dabo ne tun kafin Sufeta Janar na yanzu Kayode Egbetokun ya karɓi jagoranci.

Mai magana da yawun rundunar Olumuyiwa Adejobi ne ya bayyana hakan a cikin wani bayani da ya fitar, inda yace bata gari ne suka sace makaman lokacin hatsaniya.

Yace rundunar ta yi duk kokarinta wajen kwato makaman kuma tuni wasu suka dawo hannun rundunar.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp