Tsohon shugaban kasa na mulkin soja, Janar Ibrahim Badamasi Babangida ya ce marigayi Basorun Moshood Kashimawo Olawale Abiola ne ya lashe zaben shugaban kasa da aka gudanar a ranar 12 ga watan Yunin shekarar 1993.
IBB ya bayyana hakan ne a cikin littafin tarihin rayuwarsa mai suna “A Journey in Service” wanda aka kaddamar a Abuja ranar Alhamis.
Tsohon mataimakin shugaban kasa, Farfesa Yemi Osibanjo wanda ya duba littafin ya ruwaito Babangida na cewa Marigayi MKO Abiola ne ya samu rinjayen kuri’u a lokacin zaben.
Idan zaku tuna abaya dai tsohun shugaban kasa Muhammadu Buhari ya karrama Abiola da lambar girma ta GCFR.
Category
Siyasa