Majalisar wakilan Nijeriya ta yi kira ga ministan sadarwa, Bosun Tijani da hukumar sadarwa ta NCC, da su dakatar da karin kudin sadarwa a kasar

 

'Yan majalisar wakilai

Wannan ya biyo bayan amincewa da kudurin dan majalisar wakilai Obuku Offorji ya gabatar a zauren majalisar a ranar Talata.  

Da yake gabatar da kudirin, ya tunatar da cewa, bayan taron masu ruwa da tsaki a ranar Laraba, 8 ga watan Janairu, ministan ya bayyana cewa nan ba da jimawa ba kamfanonin sadarwa a Nijeriya za su kara farashin kudin sadarwa. 

A cewar ministar, ana ci gaba da tuntubar juna tare da wasu kamfanonin sadarwa a kasar kan karin kudin.

Sai dai ya ce ba za a yi karin kashi 100 ba, kuma hukumar NCC za ta amince da sabon tsarin da za a sanar a gaba.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp