Kaso 67 cikin 100 na waɗanda suka rubuta jarabawar NABTEB ta shekarar 2024 sun samu kyakkyawan sakamako- Hukumar NABTEB

Tambarin hukumar NABTEB 

Hukumar shirya jarabawar NABTEB ta fitar da sakamakon jarabawar da aka yi a watannin Nuwamba zuwa Disambar shekarar 2024, inda sama da kaso 67 cikin 100 na waɗanda suka rubuta suka lashe darusa biyar-biyar zuwa sama.

Mukaddashin magatakardan hukuma Dr. Nnasia Asanga, ne ya sanar da hakan ranar a Benin. 

Yace mutane dubu 44 da 226 ne suka rubuta jarabawar, yayin da dubu 29 da 880 daga cikinsu suka samu duk abinda ake bukata.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp