Hukumar Zaben Nijeriya na son ayi dokar da za ta hana zuwa da sama da naira dubu 50 a rumfar zabe


Hukumar zabe mai zaman kanta a Nijeriya INEC ta bukaci majalisa ta yi dokar haramta zuwa da kudade masu yawa a rumfunan zabe domin magance matsalar sayen kuri'a da kuma magudin zabe.

Daraktan sashen dokoki na hukumar Tanimu Muhammed, SAN, ne ya yi wannan kiran a yayin wani taron kan sake gyaran dokokin zabe da kwamitin majalisar wakilai kan zabe ya shirya a Abuja.

Tanimu Muhammed ya bukaci 'yan majalisa da su fito da dokar da zata saka naira dubu hamsin a matsayin mafi karancin kudin da mutum zai iya rika wa a kusa da rumfunan zabe.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp