Gwamnatin tarayya ta bukaci ‘yan kasuwa da su rage farashin kayan abinci

 


Ministan Noma da albarkatun kasa Abubakar Kyari ne ya bayyana bukatar hakan a ranar Talata, a yayin wani bikin noman alkama da aka gudanar a kauyen Dabi dake karamar hukumar Ringim ta jihar Jigawa.

Ministan ya bayyana takaicinsa kan yadda wasu 'yan kasuwa suka ki sauke farashi duk da saukowar kayayyaki, yana mai bayyana hakan a matsayin rashin kishin ƙasa.

Ya ce gwamnatin tarayya tana sane da saukar farashin kayan abinci a wasu manyan kasuwanni, musamman na kayan masarufi kamar su gari, sukari, shinkafa da taliya.

Amma duk da haka wasu, masu yin burodi, da masu shaguna a cikin Unguwanni sun ki sauke farashin kayyayyakin amfanin yau da kullum, a saboda haka ya yi kira da su sauke farashi kamar yadda yake sauka a wasu kasuwanni.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp