Gwamnatin jihar Sokoto za ta kashe Naira milyan 998 domin ciyarwa a cikin azumin watan Ramadan

Ahmad Aliyu

Gwamnatin jihar Sokoto ta ware sama da Naira miliyan 998 domin shirin ciyarwar watan azumin Ramadan na shekarar 2025.

Gwamnan jihar Ahmed Aliyu, a yayin kaddamar da shirin, ya jaddada kudirin gwamnatin na fadada shirin domin isa ga al'umomin jihar baki daya. 

Ya ce ko a shekarar da ta gabata irin wannan aiki na ciyarwa a cibiyoyi sama da 130 a fadin jihar.

A cewar sa a wannan shekarar a kara adadin zuwa cibiyoyi 155 don rage cunkoson wuraren da ake da su tare da tabbatar da saukin samun abinci ga masu azumi.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp