Gwamnan Rivers Sim Fabura ya biya wa mutane 67 kudin aikin hajjin 2025


Da yake zantawa da Hajj Reporters, shugaban riko na hukumar alhazzai musulmai ta jihar Abdulrazaq Diepriye ya ce, gwamnan ya biya kudin mutanen tare da tallafin da zai taimaka musu wajen yin aikin hajjin 2025.

Diepriye ya kuma bayyana cewa Gwamna Fubara ya biya wa kudin ne kafin wa’adin da hukumar NAHCON ta sanya ya cika.

A cewarsa, ko a shekarar da ta gabata gwamnan ya biya wa wasu mutanen kujerun aikin hajji domin su sauke farali.


 

1 Comments

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp