Gwamnan Katsina ya kashe naira biliyan 5.7bn domin tallafawa kiwon awaki ga mata 3,610

 



Gwamnatin jihar Katsina ta kashe naira biliyan 5.4 don tallafa wa mata 3,610 su yi kiwon awaki a fadin jihar, kowacce ta samu akuya hudu.

Gwamna Dikko Radda ya bayyana haka ne a lokacin kaddamar da rabon tallafin a karkashin shirin kiwon akuya a Dan Nakolo da ke karamar hukumar Daura.

Gwamnan ya bayyana cewa wannan bikin wani gagarumin ci gaba ne a harkar noma a jihar, kuma wani mataki ne na tabbatar da aniyar ganin jihar Katsina ta zama jagora a fannin dogaro da kai a fadin yankin Arewa da Nijeriya baki daya. 

A cewarsa, shirin bayar da akuyoyin wani muhimmin bangare ne na dabarun bunkasa kiwon dabbobi, da inganta samar da abinci da samar da dama mai dorewa ga manoma.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp