![]() |
Abba Kabir Yusuf/Aminu Abdussalam |
Gwamna Abba Kabir Yusuf ya sanya hannu a kan dokar ne a yayin zaman majalisar zartaswa ta jihar da ya gudana a ranar Talata 18/2/2025.
Hakan na zuwa ne makwanni biyu bayan majalisar dokokin jihar Kano ta zartar da kuduri bayan yin mahawara mai zurfi akan kudurin.
A cikin wasu tanade tanaden dokar, ta baiwa rundunar tsaron damar yakar miyagun laifuka, za kuma su gudanar da ayyukansu a fadin jihar.
Sanya hannu kan dokar shi ne mataki na karshe na tabbatar da ita a hukumance yayin da ake sa ran hukumomi za su sanar da tsarin daukar ma'aikatan rundunar, da kuma nadin wadan da za su jagoranci rundunar.