Bello Turji na ci gaba da neman maboya yayin da sojoji ke fatattakar 'yan bindiga


Babban hafsan sojin kasa na Nijeriya, Laftanar Janar Olufemi Oluyede, ya sha alwashin cewa nan ba da dadewa ba za a kawar da fitaccen shugaban ‘yan fashin dajin nan da ya addabi yankin arewacin Nijeriya, Bello Turji.

Olufemi Oluyede ya bayyana hakan ne a ranar Alhamis a Gusau, babban birnin jihar Zamfara, yayin da yake ganawa da manema labarai a hedikwatar Operation Hadarin Daji.

Ya ce ‘yan ta’addan da ake nema ruwa a jallo irin su Bello Turji suna ci gaba da buya, duba da irin wutar da suke sha, kuma duk inda suka je sai an kawar da su.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp