Ƙasa da kashi 30% na ‘yan Nijeriya ne ke biyan haraji ga gwamnatin tarayya - Godswill Akpabio


Shugaban Majalisar Dattawan Nijeriya, Godswill Akpabio ya bayyana cewa kasa da kashi 30% ne na yan kasar ke biyan haraji ga gwamnatin tarayya.

Shugaban Majalisar ya ce kuma a haka 'yan ƙasar ke tsammanin gwamnati za ta samar masu da ababen more rayuwa da sauran muhimman ayyuka.

Jaridar Punch ta ruwaito Godswill Akpabio ya bayyana hakan a ranar Litinin a wajen bude taron jin ra’ayin jama’a kan kudirin gyaran haraji da shugaban kasa Bola Tinubu ya aikewa majalisar.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp