An sace kananan yara kusan 20 a Maradun a jihar Zamfara

 

Dauda Lawal Gwamnan jihar Zamfara
 

Lamarin ya faru da safiyar Lahadi, a lokacin da yaran suka je itacen girki a kusa da babban asibitin garin.

Wani dan garin na Maradun da ya nemi a sakaya sunansa, ya tabbatar wa da DCL Hausa cewa, maharan sun je da muggan makamai a bisa babura a lokacin da suka sace yaran.

Rundunar 'yan sandan jihar Zamfara ta hannun kakakinta,Yazid Abubakar ta ce za ta bincika ta sanar da DCL Hausa. Har lokacin hada wannan labarin ba ta sanar da mu ba.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp