Alawar yara mai sanya maye ta fara bazuwa a sassan Nijeriya in ji hukumar NDLEA mai yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi

 

NDLEA

Jami’in hulda da jama’a na hukumar, ASN Sadiq Muhammad Maigatari, ya bayyana hakan a wata hira da yayi da manema labarai a Kano, ya ce wayar da kan iyaye ya zama wajibi su duba irin alewar ake kaiwa unguwanninsu.

Ya ce an kama alewar "Choculate" amma a cikinta ana zargin an lullube ta da abubuwan da ke sanya maye.

Maigatari ya ce ana zargin ana sayar da alewa a unguwanni ga yaran da ba su sani ba, a lokacin da za su je makaranta, ya kuma bukaci iyaye da su rika lura da wasu dabi’u da ‘ya’yansu ke nunawa a unguwanni da cikin gidajen su.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp