Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta bankado wani shiri na ‘yan ta’adda na kai hari a wuraren taruwar jama’a da wasu muhimman wurare a fadin jihar.
Wannaan dai na a cikin wata sanarwa da kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Abdullahi Kiyawa ya fitar, ya bukaci jama’a da su yi taka-tsan-tsan tare da kaucewa wuraren cunkoson jama’a.
A cewar kakakin, rundunar na a cikin shirin ko ta kwana domin murkushe bata gari.
Category
Labarai