'Yan Nijeriya za su ci ribar sauye sauyen tattalin arziki da shugaba Tinubu yazo da shi - Shugaban Majalisar dattawa sanata Godswill Akphabio

 

Sanata Godswill Akphabio

Shugaban majalisar dattawan Nijeriya, Sanata Godswill Akpabio, ya bukaci ‘yan kasar da su yi imani da sauye sauyen tattalin arzikin da shugaba Bola Tinubu ya zo da shi, yana mai cewa nan gaba za su ci riba.

Akpabio ya bayyana hakan ne a wajen wani taro a Jos, babban birnin Jihar Filato.

Shugaban majalisar dattawan wanda Sanata mai wakiltar Filato ta Arewa ya wakilta, Mwadkon Dachungyang, ya ce idan al'ummar Nijeriya suka ci gaba da hakuri da sauye sauyen tattalin arzikin shugaba Tinubu za a samu sauyi a nan gaba.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp