![]() |
Muhammad Buhari |
Buhari ya bayyana haka ne a dakin taro na Banquet Hall da ke fadar gwamnatin jihar Katsina, a yayin taron masu ruwa da tsaki na jam’iyyar APC gabanin zaben kananan hukumomin jihar a ranar 15 ga watan Fabrairu.
Tsohon shugaban kasar ya ce wadannan abubuwa na da matukar mahimmanci wajen samun daidaito a tsakanin al'umma da shugabanni da ke jagorantar su a dukkan matakai.
A nasa bangaren, Gwamna Dikko Radda, ya ce jihar ta kuduri aniyar gudanar da zabe na gaskiya, sai dai gwamnan ya umurci masu ruwa da tsaki na jam'iyyar APC a jihar da su hada kai don tabbatar da nasarar jam'iyyar.