Sojojin Nijeriya sun yi dirar mikiya mafakar Bello Turji sun hallaka ɗansa tare da banka wuta ga maɓoyarsa


Dakarun sojin Nijeriya sun tarwatsa maboyar kasurgumin dan bindiga Bello Turji tare da lalata rumbun ajiyar abincinsa da kuma hallaka dansa daya.

Mai bin diddigi da lura da al'amurran tsaro a yankin Tabkin Chadi Zagazola Makama ne ya tabbatar da hakan a shafinsa na X, kamar yadda jaridar Dailytrust ta ruwaito.

Makama yace rundunar hadaka ta Operation Fansan Yamma ce ta kai farmakin ta sama da kasa a maboyar Turji dake Fakai, cikin karamar hukumar Shinkafi ta jihar Xamfara State.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp