Sojojin Faransa za su fara ficewa daga kasar Côte d'Ivoire


Shugaban kasar Ivory Coast, Alassane Ouattara ya sanar da cewa sojojin kasar Faransa za su fara ficewa daga kasar nan ba da jimawa ba.

A cikin wani jawabin sabuwar shekara da ya yi a gidan talabijin na kasar, Ouattara ya ce sojojin Faransa 600 da ke cikin kasar za su fara barin kasar a watan Janairun da muke ciki.

Ya kara da cewa za a hannunta mazaunin sojojin ga rundunar sojin kasar Côte d'Ivoire tare da kara zamanantar da aikinsu.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp