![]() |
Shugaba Tinubu |
Mataimaki na musamman ga shugaban kasar kan harkokin yada labarai, Bayo Onanuga, ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a ranar Asabar.
Taron wanda gwamnatin Tanzaniya ta shirya tare da hadin gwiwar bankin raya Afirka da bankin duniya, zai mayar da hankali kan shirin samar da wutar lantarki ga mutane miliyan 300 a Afirka nan da shekarar 2030.
A yayin taron shugabannin kasashen Afirka da shugabannin kamfanoni masu zaman kansu, kungiyoyin farar hula, za su tsara dabarun kara samar da makamashi a Nahiyar Afirka.